
Shirin kai Tsaye
Qausain TV tashar talabijin ce da aka kafa bisa hangen nesa na Nasir Musa Idris (Albani Agege), domin yada shirye-shiryen da suka kunshi tarbiyya, ilimi, al’adu da nishadi cikin tsari mai ma’ana da daidaito. An kaddamar da tashar a hukumance a shekarar 2021, inda take watsa shirye-shiryenta ta hanyar tauraron dan adam zuwa sassa daban-daban na Najeriya da wajen ta. Tare da jajircewa wajen ci gaba da bunkasa harkar yada labarai da nishadantarwa, Qausain TV na ci gaba da haɗa karfi da fasahar zamani ta dijital, yayin da take bin sawun ginshikan da suka kafa tubalin wannan tashar mai albarka..


Manufar mu
Kare manufar wanda ya kafa Qausain TV ta hanyar yada shirye-shiryen da suka cika da tarbiyya, daidaito, da al’adunmu — domin ilmantarwa, faɗakarwa da nishadantar da al’umma.
Ganiyar Mu
Mu zama babban dandamalin watsa labarai da ke ciyar da tunani gaba, ɗaukaka dabi’u, tare da haɗa al’umma ta hanyar shirye-shiryen da ke da armashi, ilimi, da kuma dacewa da al’adu.

Aikinmu
Aikinmu shi ne ƙirƙirar shirye-shirye masu tarbiyya, ilimi da nishadi waɗanda ke inganta rayuwar al’umma, ƙarfafa ruhin mutum, da bunƙasa tunani cikin gaskiya, al’ada da daidaito.

Aikinmu
Aikinmu shi ne ƙirƙirar shirye-shirye masu tarbiyya, ilimi da nishadi waɗanda ke inganta rayuwar al’umma, ƙarfafa ruhin mutum, da bunƙasa tunani cikin gaskiya, al’ada da daidaito.
Ganiyar Mu
Mu zama babban dandamalin watsa labarai da ke ciyar da tunani gaba, ɗaukaka dabi’u, tare da haɗa al’umma ta hanyar shirye-shiryen da ke da armashi, ilimi, da kuma dacewa da al’adu.

Manufar mu
Kare manufar wanda ya kafa Qausain TV ta hanyar yada shirye-shiryen da suka cika da tarbiyya, daidaito, da al’adunmu — domin ilmantarwa, faɗakarwa da nishadantar da al’umma.
An kafa Qausain TV ne ta hannun Nasir Musa Idris (Albani Agege), wanda ya shimfiɗa tubalin kafuwar tashar a shekarar 2021 da hangen nesa na gina kafar watsa labarai mai cike da dabi'u, al'adu, da ilmantarwa.